Adedibu Ya Ce: Gwamna Abdullahi Adamu Zai Iya Kai Nijeriya Ga Tudun Mun Tsira
Alhaji Adebibu ya ce gadojin ha]in kai da kyakkyawar dangantaka da Gwamna Abdullahi Adamu ya gina a tsakanin ‘yan Nijeriya a shekara -da- shekaru a yanzu za su kasance masa matakala na kaiwa ga kujerar shugabancin }asar nan.
Cif Adedibu ya bayyana haka ne, lokacin da Gwamna Adamu ya kai masa ziyarar ban girma a gidansa da ke garin Ibadan.
Alhaji Adebibu ya bayyana Gwamna Adamu a matsayin "]alibi mai biyayya" ga shugaba Olusegun Obasanjo inda ya ce, irin wannan biyayya da gwamnan ya nuna ya jawo masa }auna da girmamawa daga magoya bayan wannan gwamnati. Ya ce, Gwamna Adamu ya mallaki basira da }arfin himmar da zai ciyar da Nijeriya gaba kamar yadda shugaba Obasanjo ya aza harsashin haka.
Sai ya ce, "Ina ro}on Allah cikin rahamarSa Ya sanya ka cikin mutanen da Zai ba su amanar ri}on }asar nan a shekara ta 2007, wannan ita ce addu’armu gare ka. Kuma a namu ~angare a shirye muke mu bayar da tamu gudunmawar."
Shi ma da yake magana kan takarar Gwamna Adamu tsohon gwamnan tsohuwar Jihar Oyo Dokta Omololu Olunloye ya ce "Gwamna Adamu ]an takarar shugaban }asa ne da ya cancanta, wanda kuma na san shi fiye da shekara 30. Shi }wararre ne kuma fitaccen ]an siyasar da ya dace ya shugabanci tarayyar Nijeriya."
Dokta Olunloye ya yi al}awarin nema wa gwamnan goyon baya a yankin Kudu maso Yamma, ta hanyar bayyana musu kyawawan halayensa da nasarorin da ya samu.
Gwamnan ya kai ziyarar gidan gwamnati da ke Badun a inda ya sadu da gwamnan Jihar Oyo, Cif Bayo Alao Akala don bayyana bu}atarsa ga al’ummar Kudu maso Yammacin }asar nan, na neman su za~e shi.
Dokta Abdullahi Adamu ya ce, yana so ya shugabanci }asar nan ne don }arfafa ha]in kai da kawo ci gaba cikin hanzari.
Ya jaddada cewa, Nijeriya ta da]e tana fama da koma baya, amma sake haye mulki da shugaba Olusegun Obasanjo ya yi a shekarar 1999, an samu ci gaba mai ma’ana.
Gwamna Bayo Akala ya tabbatar wa gwamna cewa, al’ummar Jihar Oyo da kuma Yarbawa sun gamsu da yun}urinsa na neman shugaban }asa a matsayinsa na ginshi}in ha]a kai, tare da bayyana cewa, zai za~e shi don haye kujerar shugabancin }asar nan.
Gwmanan Abdullahi Adamu har ila yau, ya kai ziyarar ban girma ga fadar Olubadan na Ibadan da Alafin na Oyo, a inda ya bu}aci sanya albarkarsu, don cimma burinsa na kasancewa shugaban }asar nan.
Sarakunan gargajiyar guda biyu, sun yaba wa gwamnan saboda biyayya da kuma goyon bayansa ga shugaba Obasanjo, inda suka tabbatar masa da goyon bayansu.
A fadar Ooni na Ife, babban basaraken }asar Yarbawan Oba Okunade Sijuwade Olubuse II, wanda ya yi magana ta bakin jami’in hul]a da jama’arsa Funmilayo Olorunshola, ya ce Gwamna Adamu mutum ne abin dogaro a kowane lokaci, don haka ba ya da shakka kan zai iya bun}asa }asar nan idan ‘yan Nijeriya suka za~e shi a matsayin shugaban }asa.
Ooni na Ife ya ce, a matsayinsa na mai ri}e da sarautar Aare Obateru na }asar Ife, Gwamna Adamu ya zama ]a ga al’ummar Ife kuma wani }usa a fadar masarautar Ife.
Da yake mayar da jawabi Gwamna Adamu ya ce, ya je Ife ne don halartar bikin al’adu na shekara- shekara na Ife, kuma ya ce, Ooni na Ife yana ba shi shawarwarin da suke ]ora shi bisa gwadaben kirki a kodayaushe.
Ya kuma ce baya ga halartar bikin ya je birnin mai tsohon tarihi ne don shaida wa basaraken }udurinsa na neman shugabancin }asar nan tare da neman sanya albarka da yin addu’a daga sarkin.
Tuesday, November 28, 2006